Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya amsa gayyatar da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta yi masa.
Wata sanarwa da ofishinsa na yaɗa labarai ya fitar ranar Laraba, ya ce Bello ya ɗauki matakin amsa gayyatar ne bayan shawara da lauyoyinsa da iyalansa da kuma abokansa na siyasa.
A watan Afrilu ne, EFCC ta ayyana neman Yahaya Bello bayan kin amsa gayyatar da ta sha yi masa da kuma tsallake yunkurin kama shi.
EFCC na tuhumar Bello da zargin halasta kuɗin haram da suka kai naira biliyan 80.2.
Ya samu rakiyar manyan ƴan Najeriya zuwa ofishin hukumar.
“Muna fatan hukumar za ta gudanar da aiki bisa kwarewa da kuma mutunta ƴancinsa a matsayin ɗan ƙasa,” in ji sanarwar.