Kungiyar ‘Rescue Nigeria Mission’, wata kungiyar siyasa dake neman goyon bayan Gwamna Yaha Bello na jihar Kogi ya zama shugaban kasa a 2023, ta ce gwamnan ba zai janyewa wani dan takara ba gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress.
Bello na daya daga cikin ‘yan takarar farko da suka bayyana sha’awar tsayawa takarar shugabancin kasa a 2023 a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress.
APC na da ‘yan takara sama da 20 da suka hada da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo (SAN); Jagoran jam’iyyar APC na kasa, kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, yana fafatawa a zaben tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar.
Abdullahi Shuaibu Damati, yayin wani gangami da aka gudanar a ranar Asabar a Abuja, domin nuna goyon bayansa ga Bello, gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar APC, ya ce gwamnan ba zai yi wa magoya bayansa kunya ba saboda wani dalili.