Ƙaramin Ministan Harkokin Waje a Najeriya Zubairu Dada ya yi ƙarin bayani game da kuɗin da za a kashe na dala miliyan takwas da rabi kwatankwacin Naira biliyan 3.5, wajen kwashe ‘yan ƙasar da yaƙi ya kora daga Ukraine.
Ya ce daga cikin ayyukan har da kula da waɗanda suka ƙi yarda su koma gida.
“Kar ku manta cewa aikin ya ƙunshi kula da ‘yan Najeriyar da babu mamaki ba za su yarda su dawo ba, da kuma sauran ayyukan ciyarwa da ofisoshin za su yi. Za mu yi sawu da yawa da ake buƙata” a cewarsa.
“Kuma su ma kansu ofisoshin suna cikin tsananin buƙata…hatta ofishin jakadancimu na Ukraine sai an ɗauke shi daga ƙasar.
“Saboda haka idan akwai wani ɗan Najeriya da aka bari a ƙasar, za mu ci gaba da yi masa addu’a kar wani abin ƙi ya same shi.”
Wani bidiyo da babban jami’in ma’aikatar harkokin waje ta Najeriya ya wallafa a shafinsa na Twitter ya nuna ‘yan ƙasar na ƙoƙarin hawa jirgin da gwamnati ta tura musu a Warsaw na Poland ranar Alhamis.