A jihar Kano yanayin hazo ya kawo tsaiko ga harakokin jama’a na yau da kullum a cikin ‘yan kwanaki nan.
Wannan lamari ya sa har ana karkatar da saukar wasu jirage a babban birnin jihar zuwa wasu wurare a ranar Lahadi, yayin da kuma yana hana wasu fitowa.
Wani mazaunin Kano, malamin makaranta , Muhammad Lawalli Abdu, ya shaida wa BBC cewa akwai sanyi da hazo a garin na Kano, lamarin da ya sanya mutane da dama ke fama da mura.
Dr. Abubakar Maina Waziri , kwararren likita a Asibitin Dala da ke Kano, ya ce ana samun yaduwar cututtuka da suka hada da tari da mura da ciwon wuya da kuma ƙaruwar tashin ciwon Asthma, ” Ya kamata idan mutane za su fita su riƙa amfani da takunkumin kariya.