Ƴan bindiga sun kutsa kasuwar wani ƙauye da ake kira Yar Bulutu da ke ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto inda suka hallaka ƴan sanda da fararen hula.
Bayanai sun ce an cikin mutanen da aka kashe akwai ƴansanda uku da kuma fararen hula.
Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar kudancin Sabon Birni a majalisar dokokin jihar Sokoto ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa maharan sun isa ƙauyen ne a kan babura kimanin 20.
Ya ƙara da cewa ƴan bindigan sun kuma ƙona mota tare da gawarwakin ƴansandan da suka kashe.
Sabon Birni na daga cikin yankunan jihar Sokoto da ke fama da hare-haren ƴan bindiga, masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.