Masu zanga-zanga sun fara fitowa a birnin Legas ranar Juma’a, rana ta biyu ta zanga-zanga kan matsin rayuwa da ake gudanarwa a Najeriya.
Masu zanga-zangar sun taru ne a unguwar Ojota riƙe da alluna masu ɗauke da saƙo daban-daban.
Zanga-zangar wadda aka fara ta a jiya Alhamis, masu yin ta sun ce sun fito ne domin nuna fushinsu kan matsin tattalin arziƙi.