Majalisar dattijai ta sanar da jingine tattaunawa kan ƙudurin sauye-sauye ga dokar haraj, wadda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya gabatar mata.
Majalisar ta ɗauki wannan matsaya ce a yau Laraba a lokacin muhawararta a zauren majalisar da ke Abuja.
Hakan na zuwa ne kwana ɗaya bayan da gwamnatin ƙasar ta umarci ma’aikatar shari’a ta ƙasar ta yi aiki tare da Majalisar Dokokin domin samun masalaha kan wasu ɓangarori na dokar da ake taƙaddama a kai.
Tattaunawa kan ƙudurin ya janyo zazzafar muhawara a faɗin Najeriya, yayin da wasu ɓangarorin ƙasar suka yi zargin cewa an cusa wasu abubuwa da za su cutar da wasu yankunan ƙasar.
A yanzu Majalisar ta umarci kwamitin da ta miƙa wa ƙudurin da ya jingine duk wani nazari a kansa, yayin da aka kafa wani kwamiti wanda zai yi aiki tare da ma’aikatar shari’a ta ƙasar domin duba ɓangarorin ƙudurin da ake taƙaddama a kai.