fidelitybank

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Date:

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar hukumar Bokkos na jihar Filato, inda suka hallaka mutum biyu tare da ƙona gidaje da kuma coci-coci.

An kai harin ne da tsakar dare ɗauke da manyan makamai waɗanda suka zarta na ƙungiyar ƴan sintiri da ke yankin.

Shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasun Fudang ya bayyana mutane biyun da aka kashe ma’ikata ne a wani coci, inda ya ce an kuma ƙona gidaje da dama da kuma coci-coci, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Fudang ya ce maharan sun kuma lalata gonaki sannan suka yi awon gaba da shanu da tumakai da awakai da agwagi har ma da abincin da aka adana.

“Sun zo ne ta hanyar Ding’ak da Kopmur duk da cewa akwai shingen binciken jami’an tsaro a wajen. Sojoji sun yi harbi a iska sai dai ba su fafata da maharan ba,” kamar yadda Fudang ya yi zargi.

Shugaban al’ummar ta Bokkos ya ce harin na zuwa ne kwanaki biyu da kai irin makamancinsa a al’ummar Ndimar – Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da kuma ta jihar da su kai musu ɗaukin gaggawa tare da ganin an hukunta waɗanda ke far musu.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp