Shugaban kwamitin riko da tsare-tsare na babban taron jam’iyyar APC, kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce, ayyukan da kwamitin kula da tsare-tsare, ya sanyawa jam’iyyar kwarin gwiwa gabanin babban taronta na kasa da aka shirya gudanarwa a ranar 26 ga Maris.
Da yake karbar bayanin shugaban kwamitin kuma gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje tare da sauran mambobin kungiyar a daren Asabar, Buni ya bayyana cewa, kwamitin ya ja kunnen ‘ya’yan jam’iyyar masu ra’ayin mazan jiya da cewa babban taron ta a ranar da aka tsayar ya na nan.
Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba ya fitar, wadda PlatinumPost ta samu ta rawaito cewa, Buni na tabbatar da cewa, jam’iyyar ta shirya babban taro wanda ya kira hadin gwiwar dukkan mambobin jam’iyyar.
Shugaban ya yabawa kwamatin da ya ce, suna gudanar da ayyukan da suka dace, wajen ganin an gudanar da babban taron jam’iyyar.
Buni ya ce, kwamitin shi ne na biyu a kan babban kwamitin tsare-tsare na taro bisa la’akari da muhimmancinsa, wanda ya sanar da nadin Gwamna Ganduje ya shugabance shi tare da wasu jiga-jigan mambobin da ke da tarihin nasarori a ayyukansu.
Ya kuma bukaci kwamitin da ya yi aiki tare da sauran kwamitoci musamman ofishin kula da harkokin gwamnati da ke Abuja, duba da yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo za su halarci taron.
Tun da farko, shugaban kwamitin kula da ka’idoji, Gwamna Ganduje, ya bayyana cewa, an kammala daukar matasa maza da mata aiki a matsayin jami’an yarjejeniya da basu horo a wani bangare na aikin kwamitin.
Ya ce kwamitin ya kuma dukufa wajen samar da wani shiri na abubuwan da suka faru,bdomin samun nasarar babban taron jam’iyyar.
Gwamna Ganduje ya kuma mika godiyarsa ga Buni tare da yin alkawarin yin aiki da sauran kananan kwamitoci, domin ganin an shirya babban taro cikin nasara.