fidelitybank

Yadda kwamitin Ganduje ya cusa kwarin gwiwa a APC – Buni

Date:

Shugaban kwamitin riko da tsare-tsare na babban taron jam’iyyar APC, kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce, ayyukan da kwamitin kula da tsare-tsare, ya sanyawa jam’iyyar kwarin gwiwa gabanin babban taronta na kasa da aka shirya gudanarwa a ranar 26 ga Maris.

Da yake karbar bayanin shugaban kwamitin kuma gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje tare da sauran mambobin kungiyar a daren Asabar, Buni ya bayyana cewa, kwamitin ya ja kunnen ‘ya’yan jam’iyyar masu ra’ayin mazan jiya da cewa babban taron ta a ranar da aka tsayar ya na nan.

Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba ya fitar, wadda PlatinumPost ta samu ta rawaito cewa, Buni na tabbatar da cewa, jam’iyyar ta shirya babban taro wanda ya kira hadin gwiwar dukkan mambobin jam’iyyar.

Shugaban ya yabawa kwamatin da ya ce, suna gudanar da ayyukan da suka dace, wajen ganin an gudanar da babban taron jam’iyyar.

Buni ya ce, kwamitin shi ne na biyu a kan babban kwamitin tsare-tsare na taro bisa la’akari da muhimmancinsa, wanda ya sanar da nadin Gwamna Ganduje ya shugabance shi tare da wasu jiga-jigan mambobin da ke da tarihin nasarori a ayyukansu.

Ya kuma bukaci kwamitin da ya yi aiki tare da sauran kwamitoci musamman ofishin kula da harkokin gwamnati da ke Abuja, duba da yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo za su halarci taron.

Tun da farko, shugaban kwamitin kula da ka’idoji, Gwamna Ganduje, ya bayyana cewa, an kammala daukar matasa maza da mata aiki a matsayin jami’an yarjejeniya da basu horo a wani bangare na aikin kwamitin.

Ya ce kwamitin ya kuma dukufa wajen samar da wani shiri na abubuwan da suka faru,bdomin samun nasarar babban taron jam’iyyar.

Gwamna Ganduje ya kuma mika godiyarsa ga Buni tare da yin alkawarin yin aiki da sauran kananan kwamitoci, domin ganin an shirya babban taro cikin nasara.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp