fidelitybank

Yadda Ganduje ya miƙa mulki ga NNPPP

Date:

Gwamnatin jihar Kano, ƙarƙashin Abdullahi Umar Ganduje mai barin gado ta gabatar da rahoton miƙa mulki ga zaɓaɓɓen gwamnan jihar, Injiniya Abba Kabir Yusuf.

A wani ɗan taƙaitaccen taro da aka yi a Fadar gwamnati, Ganduje wanda ya sami wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji ya nanata ƙudirinsa na tabbatar da miƙa mulki salin alin ba tare da matsala ba.

Ya buƙaci gwamnati mai jiran gado ta yi nazari kan rahoton sannan ta gabatar da tsokacinta.

A nasa jawabin, zaɓaɓɓen gwamnan na Kano da ya samu wakilcin shugaban kwamitin karɓar mulki na Jam’iyyar NNPP, Dr Abdullahi Baffa Bichi, ya bayyana cewa kwamitin zai bai wa gwamna mai jiran gado rahoto sannan zai sanar da tsokacinsa idan har akwai.

“A wannan lokacin, saura sa’a 105 a miƙa mulki a jihar Kano a don haka mun ƙudiri aniyar tabbatar da karɓar mulki cikin salama don ci gaban Kano da al’ummarta.”

Wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran gwamna mai jiran gado na Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ce za su fitar da bayanai game da bikin ƙaddamar da sabuwar gwamnati bayan cimma yarjejeniya tsakanin gwamnati mai ci da mai barin gado.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp