fidelitybank

Yadda EFCC ta gano Naira biliyan 30 da Beta Edu ta wawushe

Date:

Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC, ta ce ta gano Naira biliyan 30 a wajen ministar ma’aikatar jin kai da aka dakatar, Betta Edu.

Haka kuma ta ce tana gudanar da bincike kan wasu asussan banki 50 duka a cikin badakalar kuɗaɗe da aka yi a ma’aikatar.

Shugaban hukumar ta EFCC, Ola Olukoyede, ne ya bayyana haka, inda ya ce akwai buƙatar a kafa kotuna na musamman waɗanda za su lura da shari’oin zargin cin hanci.

Olukoyode ya ce kuɗaɗen da aka kwato na cikin asusun gwamnatin tarayya a halin yanzu.

EFCC dai na gudanar da binciken badakalar da aka samu a ma’aikatar jin kai da ta shafi ministar da aka dakatar, Betta Edu, da tsohuwar ministar ma’aikatar, Sadiya Umar-Farouq, da kuma Halima Shehu, shugabar hukumar ba da tallafin dogaro da kai ta ƙasa NSIPA.

A watan Janairu ne dai shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Edu sakamakon badakalar kuɗaɗe a ma’aikatar.

Daga nan ne EFCC ta kira ta domin amsa tambayoyi bayan fitar wata takarda da ta nuna cewa Betta ta ba da umarnin biyan sama da naira miliyan 585 cikin asusun ajiyar wani mutum, lamarin da ya saɓa da ƙa’idar aiki.

A cikin wata wasiƙa da aka yi zargin ministar ta sanya hannu, Betta ta umarci babbar akantar Najeriya, Oluwatoyin Madein ta zuba kuɗi cikin asusun wata mai suna Oniyelu Bridget, a matsayin tallafi ga ƙungiyoyin mutane masu rauni a jihohin Akwa Ibom da Cross River da Lagos da kuma Ogun.

Sai dai babbar akantar ta yi bayanin cewa, ko da yake ofishinta ya karɓi wannan buƙata daga ma’aikatar jin ƙai, amma bai yi abin da aka nema ba.

Betta Edu, ‘yar shekara 37, wadda ita ce matashiya mafi ƙaranci shekaru a jerin ministocin Tinubu, daga bisani ta ce ƙulle-ƙulle ne kawai ake yi don a ɓata mata suna, ta ƙara da cewa ba za ta yi almundahana da duniyar gwamnati ba

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp