fidelitybank

Yadda Boko Haram suka kashe rayuka 22 a Borno

Date:

Ƙungiyar Boko Haram mai iƙirarin jihadi ta kashe aƙalla mutum 22 a ƙarshen mako sakamakon hare-haren da mayaƙanta suka kai a arewa maso gabashin Najeriya.

A jihar Borno, mayaƙan sun yi wa wasu fararen hula kwanton ɓauna tare da kashe 10 da kuma wasu jami’an tsaro biyu a ranar Asabar, kamar yadda Sarkin Gwoza Mohammed Shehu Timta ya faɗa wa kamfanin labarai na Reuters.

A garin Kopre na jihar Adamawa ma, mayaƙan Boko Haram sun kashe mutum 10 tare da raunata wasu da yawa, a cewar mazauna yankin.

Harin ya auka kan mafarauta ne da kuma mayaƙan sa-kai na CJTF, inda daga baya rundunar ‘yansanda a jihar ta tura ƙarin dakaru, in ji mai magana da yawunta Suleiman Yahaya a yau Litinin.

Najeriya ta daɗe tana fama da mayaƙa masu iƙirarin jihadi, inda Boko Haram da Iswap suka fi kai hare-hare a jihohin Borno da Yobe da Adamawa.

A farkon makon nan ne Gwamnan Borno Babagana Zulum ya koka cewa Boko Haram ta zafafa hare-hare, abin da ke jawo koma-baya a yaƙi da ‘yanbindigar.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp