Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta zaɓi manyan ƙwararrun lauyoyi 12, domin tsaya mata a shari’ar ƙorafin da jam’iyyun adawa za su shigar domin ƙalubalantar nasarar jam’iyar a zaɓen shugaban ƙasa.
A wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar ta hannun babban mai bayar da shawara kan harkokin shari’a na jam’iyyar Ahmad El-Marzuq, ya ce tawagar lauyoyin masana fannin shari’a ne, waɗanda kuma ya ce suke da ƙwarewa kan ƙararrakin zaɓe, sannan masu cikakkiyar masaniya game da kundin tsarin mulki da dokokin ƙasa.
Ya ce tawagar manyan lauyoyin12 ƙarƙashin jagorancin fitaccen lauyan ƙasar Prince Lateef Fagbemi, za su kare nasarar da jam’iyyar ta samu a zaɓen a gaban kotu.
Manyan jam’iyyun adawar ƙasar na PDP da LP ne dai suka ce za su garzaya kotu domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasar da ya bai wa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC nasara a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar cikin watan da ya gabata.