fidelitybank

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

Date:

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin zuwa ta’aziyya da kuma jana’izar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari wanda ya rasu a ranar Lahadi 15 ga watan Yulin 2025 a birnin Landan.

Mutane da dama sun isa jihar tun a jiya Litinin, inda wasu ke Katsina domin tarbar gawar sa, yayin da wasu kuma suka wuce kai tsaye zuwa Daura inda za a yi janaizar marigayin.

Mutanen sun haÉ—a da wasu sannanu a Æ™asar ciki har da manyan Æ´an siyasa kamar tsohon gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari, tsohon shugaban ma’aikata a fadar gwamnatin shugaba Buhari Farfesa Gambari da Arc Ahmed Musa Dangiwa, sai tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El Rufai, da Sunday Dare, da mai magana da yawun Buhari Garba Shehu, sai Malam Isa Ali Pantami da kuma dai dai kun Æ´an Najeriya.

A yanzu haka gidan marigayin da kuma jihar na cike da jam’ian tsaro inda Æ´an sanda da jami’an tsaron farin kaya suka jibge É—aruruwan jam’iansu.

Rahotanni na cewa bayan an kawo mamacin, za a soma kai shi gidan sa da ke Daura domin yan uwa su yi masa adduoi, daga nan a kai shi fadar mai martaba sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk domin yi masa Sallah, daga bisani kuma a sake mayar da gawar gidansa domin birne sa.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp