fidelitybank

Yadda aka yi jana’izar mutane 15 da Lakurawa su ka kashe a Kebbi

Date:

An gudanar da jana’izar mutanen da Lakurawa suka kashe a garin Mera na jihar Kebbi.

A ranar Juma’a da rana ne dai aka samu arangama tsakanin mutanen gari da Lakuwaran a wajen garin Mera na jihar Kebbi.

An samu arangamar ne dai bayan da aka zargi Lakuwaran da ƙwace wa wani mutumin gari Mera dabbobin da ke yake kiwo a wajen garin, lamarin da ya sa ‘yan garin suka fusata, suka kuma fita bayan gari da nufin yin arangama da Lakuwaran domin ƙwato dabbobin.

Arangamar ta haifar da asarar rayuka da jikkata daga mutanen garin da kuma ɓangaren Lakuwaran, kamar yadda wani ɗan jarida ya tabbatar wa BBC.

Cikin waɗanda suka halarci jana’izar har da mataimakin gwamnan jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida tare da Maimartaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama’ila Muhammad Mera.

A cikin makon nan ne dai hadikwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da ɓullar ƙungiyar Lakurawan, bayan da mazauna yankin suka koka game da ayyukan ‘yan ƙungiyar, waɗanda ke ƙwace wa mutane dabbobi da nufin samun ”ganima” ko fitar da ”zakka”.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp