An gudanar da jana’izar mutanen da Lakurawa suka kashe a garin Mera na jihar Kebbi.
A ranar Juma’a da rana ne dai aka samu arangama tsakanin mutanen gari da Lakuwaran a wajen garin Mera na jihar Kebbi.
An samu arangamar ne dai bayan da aka zargi Lakuwaran da ƙwace wa wani mutumin gari Mera dabbobin da ke yake kiwo a wajen garin, lamarin da ya sa ‘yan garin suka fusata, suka kuma fita bayan gari da nufin yin arangama da Lakuwaran domin ƙwato dabbobin.
Arangamar ta haifar da asarar rayuka da jikkata daga mutanen garin da kuma ɓangaren Lakuwaran, kamar yadda wani ɗan jarida ya tabbatar wa BBC.
Cikin waɗanda suka halarci jana’izar har da mataimakin gwamnan jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida tare da Maimartaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama’ila Muhammad Mera.
A cikin makon nan ne dai hadikwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da ɓullar ƙungiyar Lakurawan, bayan da mazauna yankin suka koka game da ayyukan ‘yan ƙungiyar, waɗanda ke ƙwace wa mutane dabbobi da nufin samun ”ganima” ko fitar da ”zakka”.