Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da kwamishiniyar harkokin mata a Cross River, Mrs Gertrude Njar a ranar Laraba a Calabar.
Wani ganau mai suna Mista Samuel Okon ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN cewa wasu samari dauke da rufe fuska ne suka fitar da ita da karfi daga motarta.
A cewar Okon, sun tafi da kwamishiniyar ne a cikin motarsu inda suka yi watsi da motarta a Calabar ta Kudu.
Mista Kalita Aruku, mai ba Gwamna Ben Ayade shawara kan harkokin yada labarai, ya tabbatar da sace ta a wata hira da NAN ta wayar tarho.
Karanta Wannan: Ana tuhumar magoya bayan Arsenal da Manchester United da kisan kai
“Eh, majiyoyin tsaro sun sanar da mu cewa an yi garkuwa da kwamishiniyar harkokin mata.
“A yayin da muke magana, jami’an tsaro sun kaddamar da farautar masu garkuwa da mutane da nufin cafke su tare da kubutar da wanda abin ya shafa ba tare da wani rauni ba,” inji shi.