Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta tabbatar da kisan shugabar mata ta jam’iyyar APC ta unguwar Koro da ke karamar hukumar Ekiti, a yayin wani aikin ceto da hadin gwiwar tawagar jami’an tsaro da ‘yan banga suka yi.
Wani jigo a jam’iyyar APC kuma dan uwan daya daga cikin wadanda abin ya shafa, Mista Adekunle Oluwole, ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labarai na NAN a ranar Lahadin da ta gabata, cewa daya daga cikin wadanda lamarin ya shafa ta rasa ranta a yayin musayar wuta da aka yi.
Ya ce, wani dan kungiyar ‘yan banga a yankin ya lura da kasancewar masu garkuwa da mutane a daya daga cikin dazuzzukan, inda suka koma gida domin karfafa musu gwiwa kafin su koma neman a sako mutanen.
Oluwole ya kuma ce, masu garkuwa da mutanen na tare da wasu mutane uku wadanda ba ‘ya’yan jam’iyyar APC ba ne, daya daga cikin mutanen na su ya samu rauni da bindiga kuma an kai su asibiti domin yi masa magani.
Ya bayyana cewa, an kuma ceto sauran mutanen da aka yi garkuwa da su tare da ‘ya’yan jam’iyyar APC yayin da aka kai wadanda suka jikkata zuwa wani asibiti da ba a bayyana ba a Osi, da kuma karamar hukumar Ekiti ta jihar.