Shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Edo, Kanal David Imuse mai ritaya, ya ce, babban zaben 2023 ya zama wajibi jam’iyyar ta samu nasara a jihar.
Imuse ya bayyana haka ne a Benin ranar Asabar yayin da yake tsokaci kan zaben fidda gwani na jam’iyyar a jihar.
Nasarar da muka samu a 2023 za ta zama share fage ga jam’iyyar APC ta kwace jihar a zaben gwamna na 2024.
“Da abin da muke gani a yanzu, a bayyane yake cewa 2023 ga APC dole ne ya ci nasara kuma ba shakka, share fage ne ga abin da zai faru a 2024.
“APC na ci gaba,” in ji shugaban.
Da yake mayar da martani game da zanga-zangar da aka yi a mazabar jihar Egor, Imuse ya ce: “’A kowane zabe, dole ne a samu wanda ya yi nasara da wanda ya fadi.