fidelitybank

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Date:

Ministar al’adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan kudancin Najeriya a wa’adin mulki mai zuwa domin tabbatar da daidaito da adalci.

Kodayake kundin tsarin mulkin Najeriya, bai yi tanadinsa ba, manyan jam’iyyun ƙasar na bin tsarin karɓa-karɓa tsakani kudanci da arewacin ƙasar.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Channels ranar Juma’a, Hannatu Musawa ta ce ya kamata mulki ya ci gaba da zama a hannun ƴan kudancin ƙasar indai adalci ake son yi.

A shekarar 2023 ne Shugaba Tinubu – wanda ɗan kudancin ƙasar ne – ya karɓi mulki daga Muhamamdu Buhari ɗan arewaci – da ya shafe shekara takwas a kan karagar mulki.

“Abu ne na fahimta, bayan shekara takwas na Buhari daga arewa ya kamata su ma ƴan kudu su yi shekara takwas, domin samar da adalci”, in ji ministar

A baya-bayan nan ma an ambato tsohon gwamnan Benue, Samuel Ortom na cewa ba zai goyi bayan ɗan takara daga arewacin ƙasar ba.

Batun karɓa-karɓa tsakanin arewaci da kudancin Najeriya, wani al’amari da aka jima ana muhawara kansa a fagen siyasar Najeriya.

Wani abu da masana ke cewa yana mayar da tsarin dimokraɗiyyar ƙasar baya.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya ba za ta karbi ‘yan ciranin Venezuela ba da Amurka za ta ba mu – Najeriya

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya ce ƙasar...

Bafarawa ya kafa sabuwar kungiya

Wasu shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki daga...

An fara shirye-shiryen aikin Hajjin badi a Najeriya

Hukumar Alhazan Najeriya ta fara shirhin aikin hajjin 2026...

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne...

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Ministar al'adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya...

Rashin abinci mai gina jiki Najeriya ce kan gaba a Afirka ta biyu a duniya

Babbar mai taimaka wa shugaban Najeriya Bola Tinubu kan...

Gwamnatin Najeriya ta ciyo bashin dala miliyan 747

Najeriya ta karɓo bashin dala miliyan 747 daga bankunan...

Ba don Tinubu ba ko zaɓen fitar da gwani Buhari ba zai ci ba

Babban mai taimaka wa Shugaba Tinubu kan kafofin yaɗa...

Majalisa ta gayyaci Gwamnan Filato kan tsaron jihar

Kwamitin wucin gadi kan matsalolin tsaron jihar Filato na...

Sojoji sun sun kashe ‘yan Boko Haram 24

Rundunar Sojoji ƙarƙashin rundunar 'Operation Hadin Kai' mai yaƙi...

Dangote zai gina rumbum man fetur da dizel a Namibia

Matatar mai ta Dangote da ke Najeriya za ta...

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...
X whatsapp