fidelitybank

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Date:

Ministar al’adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan kudancin Najeriya a wa’adin mulki mai zuwa domin tabbatar da daidaito da adalci.

Kodayake kundin tsarin mulkin Najeriya, bai yi tanadinsa ba, manyan jam’iyyun ƙasar na bin tsarin karɓa-karɓa tsakani kudanci da arewacin ƙasar.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Channels ranar Juma’a, Hannatu Musawa ta ce ya kamata mulki ya ci gaba da zama a hannun ƴan kudancin ƙasar indai adalci ake son yi.

A shekarar 2023 ne Shugaba Tinubu – wanda ɗan kudancin ƙasar ne – ya karɓi mulki daga Muhamamdu Buhari ɗan arewaci – da ya shafe shekara takwas a kan karagar mulki.

“Abu ne na fahimta, bayan shekara takwas na Buhari daga arewa ya kamata su ma ƴan kudu su yi shekara takwas, domin samar da adalci”, in ji ministar

A baya-bayan nan ma an ambato tsohon gwamnan Benue, Samuel Ortom na cewa ba zai goyi bayan ɗan takara daga arewacin ƙasar ba.

Batun karɓa-karɓa tsakanin arewaci da kudancin Najeriya, wani al’amari da aka jima ana muhawara kansa a fagen siyasar Najeriya.

Wani abu da masana ke cewa yana mayar da tsarin dimokraɗiyyar ƙasar baya.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp