fidelitybank

Ya kamata Buhari ya ɗaure ni da sauran ƴan siyasa — Tsohon Minista

Date:

 

 

 

 

Tsohon Ministan Aiyuka, Ambasada Ibrahim Musa Kazaure ya sanya kansa a cikin ƴan siyasar da ya kamata a hukunta su sakamakon zagon-ƙasa da su ka yi wa Nijeriya ta hanyar sace kuɗaɗen gwamnati.

Da a ke zanta wa da shi a wani shiri a tashar rediyo ta Radio France International, Kazaure ya ce duk ƴan siyasar Nijeriya ɗaya su ke, inda ya ce babu wani wanda ya ke yi don talakawa.

A cewar sa, ya faɗa wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da ya kame duk ƴan siyasar da su ka wawashe kuɗaɗen gwamnati har da shi.

Tsohon Ministan ya ce duk ƴan siyasan da su ka rike madafun iko tun daga 1999 ba su yi wa ƙasar komai ba.

“Har ni da na ke wannan maganar, ya kamata a ɗaure mu sabo da ba mu yi wa ƙasar nan komai ba

“Na sha faɗin cewa ni Ibrahim Musa Kazaure, mun zalunci Nijeriya da talakawan ta.

“Magana ta gaskiya ita ce, dukkan mu kanwar ja ce. Abin da mu ka yi wa Nijeriya ba haka ya dace mu yi mata ba sabo da wasu daga cikin mu sun samu dama wasu kuma basu samu ba.

“Ni dai gaskiya na faɗa. Dukkkan mu da mu ka yi sata, a matse mu mu dawo da kuɗaɗen da mu ka sata. Na faɗa wa Buhari, a kame mu a ɗaure mu har sai mun dawo da kuɗaɗen da mu ka sata.

“Ni ba zan sake karɓar wani muƙami a kasar nan ba, ko da kyauta ne,” in ji Kazaure.

 

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp