fidelitybank

Yaƙin Ukraine: Rukunin farko na ƴan Nijeriya sun isa Abuja

Date:

Kashi na farko na ƴan Nijeriya da aka kwashe daga birnin Bucharest na ƙasar Romania su ka sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a yau Juma’a da safe
Mutanen da a ka kwaso daga Ukraine sakamakon mamayar da Russia ta yi a ƙasar Ukraine sun nemi mafaka a Romania.
Gwamnatin taraiya ta baiwa kamfanin Max Air da Air Peace kwangilar kwashe ƴan Nijeriya da su ka maƙale a kan dala miliyan 8.5, bayan da a ka buƙaci su gudu zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Poland, Hungary, Romania da sauransu.
Yayin da Air Peace ba zai iya tashi daga Najeriya ba kamar yadda aka tsara, saboda wasu matsaloli, jirgin Max Air ya tashi daga Abuja zuwa Bucharest, a ranar Alhamis, kuma yanzu ya dawo da rukunin farko.
Jirgin mai lamba 747-400 mai lambar rijista 5N-HMM ya sauka a filin jirgin ne da karfe 06:11 na safiyar yau, kamar yadda wani jami’in kamfanin ya tabbatar wa wakilinmu.
Rahotanni sun baiyana cewa gwamnatin taraiya ta bada dala 100 ga kowanne ɗan ƙasar da a ka dawo da shi.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp