fidelitybank

Yaƙin Ukraine: Rukunin farko na ƴan Nijeriya sun isa Abuja

Date:

Kashi na farko na ƴan Nijeriya da aka kwashe daga birnin Bucharest na ƙasar Romania su ka sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a yau Juma’a da safe
Mutanen da a ka kwaso daga Ukraine sakamakon mamayar da Russia ta yi a ƙasar Ukraine sun nemi mafaka a Romania.
Gwamnatin taraiya ta baiwa kamfanin Max Air da Air Peace kwangilar kwashe ƴan Nijeriya da su ka maƙale a kan dala miliyan 8.5, bayan da a ka buƙaci su gudu zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Poland, Hungary, Romania da sauransu.
Yayin da Air Peace ba zai iya tashi daga Najeriya ba kamar yadda aka tsara, saboda wasu matsaloli, jirgin Max Air ya tashi daga Abuja zuwa Bucharest, a ranar Alhamis, kuma yanzu ya dawo da rukunin farko.
Jirgin mai lamba 747-400 mai lambar rijista 5N-HMM ya sauka a filin jirgin ne da karfe 06:11 na safiyar yau, kamar yadda wani jami’in kamfanin ya tabbatar wa wakilinmu.
Rahotanni sun baiyana cewa gwamnatin taraiya ta bada dala 100 ga kowanne ɗan ƙasar da a ka dawo da shi.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp