Shugaban Hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, ta yi Allah-wadai da yadda hukumomin kasar Poland ke yi da kuma tsare ‘yan Najeriya da wasu ‘yan Afirka da suka yi gudun hijira zuwa Poland bayan tserewa rikicin Ukraine.
Dabiri-Erewa ta yi magana a asibitin Psycho-social Trauma Clinic na Ukraine masu dawowa da suka shirya tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira, Baƙi da Muhallin Cikin Gida (NCFRMI).
Ta yi nuni da cewa, duk da cewa shugaba Mohammadu Buhari, ya yi duk wani shiri da ya kamata ‘yan Najeriyar da suka fada cikin halin yaki su koma gida, amma wasu sun zabi ci gaba da zama a kasashe makwabta kamar Poland.
Shugaban na NiDCOM ta ce “Mafi dacewa matakin da Poland ta dauka shi ne mayar da su kasashensu, maimakon ajiye su a wuraren da ake tsare da su,” in ji Shugaban na NiDCOM, ta kara da cewa “ba a amince da wannan dabi’ar ba kuma abin zargi ne”.
A halin da ake ciki kuma, wata sanarwa da NIDCOM ta fitar ta ce, Shugaban Daliban Najeriya da ke Ukraine, Fehintola Damilola Moses, ya yaba wa Shugaba Buhari da tawagarsa kan “amsar gaggawa da ceto daliban daga Ukraine”.