Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya jawabi ga kungiyoyin kasashen waje da ke aiki kasashen yankin tafkin Chadi da abokan hulda daga Birtaniya da kuma sauran kasashe.
Kungiyar kasashen renon Ingila ce ta shirya taron.
Taron ya mayar da hankali ne a kan hanyoyin da ake bi wajen magance rikice-rikicen kasashen yankin Tafkin Chadi da kuma yadda za a mayar da hankali wajen ganin ‘yan kungiyar Boko Haram da dama sun mika wuya.
Taron ya samu halartar sojoji da shugabannin kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da shugabannin siyasa da na jami’oi da kuma kungiyoyin agaji daga Chadi da Najeriya da Nijar da kuma Kamaru.
Za a duba irin hanyoyin da ya kamata abi wajen magance matsalolin ‘yan ta’adda da ke addabar yankin. In ji BBC.
A jawabinsa, Gwamna Zulum ya bayyana irin yadda ake yakar masu tayar da kayar baya a Borno da kuma yadda aka sake gina jihar.
Gwamna Zulum, ya kuma bayyana irin illolin da yakin Boko Haram ya haifar a Borno musamman wajen lalata gine-gine da tursasawa mutane barin muhallansu da kuma irin matsalolin ayyukan jinkai da ake fuskanta a jihar.