fidelitybank

Yaƙin Ukraine: Rukunin farko na ƴan Nijeriya sun isa Abuja

Date:

Kashi na farko na ƴan Nijeriya da aka kwashe daga birnin Bucharest na ƙasar Romania su ka sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a yau Juma’a da safe
Mutanen da a ka kwaso daga Ukraine sakamakon mamayar da Russia ta yi a ƙasar Ukraine sun nemi mafaka a Romania.
Gwamnatin taraiya ta baiwa kamfanin Max Air da Air Peace kwangilar kwashe ƴan Nijeriya da su ka maƙale a kan dala miliyan 8.5, bayan da a ka buƙaci su gudu zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Poland, Hungary, Romania da sauransu.
Yayin da Air Peace ba zai iya tashi daga Najeriya ba kamar yadda aka tsara, saboda wasu matsaloli, jirgin Max Air ya tashi daga Abuja zuwa Bucharest, a ranar Alhamis, kuma yanzu ya dawo da rukunin farko.
Jirgin mai lamba 747-400 mai lambar rijista 5N-HMM ya sauka a filin jirgin ne da karfe 06:11 na safiyar yau, kamar yadda wani jami’in kamfanin ya tabbatar wa wakilinmu.
Rahotanni sun baiyana cewa gwamnatin taraiya ta bada dala 100 ga kowanne ɗan ƙasar da a ka dawo da shi.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp