A safiyar Talata ne, babban layin wuta na ƙasa ya sake lalacewa inda ya jefa ɗimbin mutane cikin duhu.
Hakan na zuwa ne ƙasa da sa’a 24 bayan da kamfanonin rarraba wutar lantarki a faɗin ƙasar suka sanar da cewa layin ya lalace da misalin karfe 6:48 na yammacin ranar Litinin.
Wata sanarwa da kamfanin rarraba wutar lantarki a jihar Legas Eko ya fitar, ta ce an samu matsala a babban layin ne da misalin karfe 9 na safiyar yau Talata, abin da ya janyo rashin wuta ga ɗimbin mutane.
“Muna aiki tukuru tare da abokan hulɗar yayin da muke ƙoƙarin mayar da hasken wutar lantarki. Za mu sanar da mutane da zarar al’amura sun daidaita,” in ji kamfanin.