Shugaban karamar hukumar Garko, Salisu Musa Sarina, ya yabawa gwamnatin jihar Kano, bisa aiyukan raya kasa da take aiwatarwa al’ummar jihar.
Alhaji Salisu Sarina ya bayyana hakan ne yayin da kwamashinan ma’aikatar raya karkara da ci gaban al’umma na jihar Kano, Musa Iliyasu kwankwaso, ya ziyarci fadar hakimin yankin.
Shugaban karamar hukumar wanda daraktan mulki na yankin, Alhaji Halilu Kunya ya wakilta ya ce, duba da tarin ayyukan da gwamnati mai ci yanzu ta ke gudanarwa a fadin jihar nan ya zama wajibi a yaba mata.
Da ya ke nasa jawabin kwamashinan ma’aikatar raya karkara, Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso ya ce, “Mun ziyarci yankin ne, domin wayar da kan al’umma a kan shirin gwamnati na samar da hasken wuta mai amfani da hasken rana ga al’umma musamman mutanen karkara”.
Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso wanda mai taimaka masa na musamman Alhaji Abdulhamid Yusuf ya wakilta ya ce, “Shirin zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar nan, kuma shirin zai baiwa matasan yankin yadda ake gyaran kayayyakin na’ura mai amfani da hasken rana”.