fidelitybank

Wike bai yi wa ƴaƴan jam’iyyar sa gargaɗi ba a kan Atiku – PDP

Date:

Jam’iyyar PDP a jihar Ribas, ta yi watsi da ikirarin da gwamnan jihar, Nyesom Wike ya yi na cewa ya haramtawa mambobinta yin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar a jihar.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na jihar, Tambari Gbara, ya jaddada cewa, Wike bai taba haramtawa jiga-jigan jam’iyyar yakin neman zaben Wike a jihar Ribas ba.

Gbara yana maida martani ne kan ikirarin da wani tsohon Sanata mai wakiltar Ribas ta Kudu maso Gabas, Ledogo Maeba ya yi na cewa Wike ya gargadi wasu jiga-jigan jam’iyyar kan yi wa Atiku kamfen a jihar.

Maeba ya ce, Wike ya yi wannan gargadin ne bayan da shi da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka ziyarci Atiku inda suka nemi gafara a madadin gwamnan.

Tsohon dan majalisar ya ce, gwamnan ya tsawatar da su kan ziyarar Atiku ba tare da amincewar sa ba.

Maeba ya ce, Wike ya kuma yi barazanar cewa, duk wanda ya yi wa Atiku yakin neman zabe a jihar Ribas ba tare da izininsa ba za a hukunta shi.

Sai dai Gbara ya kalubalanci Maeba da ya tabbatar da zarginsa da cewa Wike ya bayar da barazana ga duk wanda ke yiwa Atiku yakin neman zabe a jihar.

A cikin wata sanarwa, Gbara ya ce: “Idan har gwamnan yana son yin wannan magana, zai bayyana a hukumance, cewa, a jihar, kada wani ya yi wa Atiku Abubakar yakin neman zabe.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp