fidelitybank

Wike bai yi wa ƴaƴan jam’iyyar sa gargaɗi ba a kan Atiku – PDP

Date:

Jam’iyyar PDP a jihar Ribas, ta yi watsi da ikirarin da gwamnan jihar, Nyesom Wike ya yi na cewa ya haramtawa mambobinta yin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar a jihar.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na jihar, Tambari Gbara, ya jaddada cewa, Wike bai taba haramtawa jiga-jigan jam’iyyar yakin neman zaben Wike a jihar Ribas ba.

Gbara yana maida martani ne kan ikirarin da wani tsohon Sanata mai wakiltar Ribas ta Kudu maso Gabas, Ledogo Maeba ya yi na cewa Wike ya gargadi wasu jiga-jigan jam’iyyar kan yi wa Atiku kamfen a jihar.

Maeba ya ce, Wike ya yi wannan gargadin ne bayan da shi da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka ziyarci Atiku inda suka nemi gafara a madadin gwamnan.

Tsohon dan majalisar ya ce, gwamnan ya tsawatar da su kan ziyarar Atiku ba tare da amincewar sa ba.

Maeba ya ce, Wike ya kuma yi barazanar cewa, duk wanda ya yi wa Atiku yakin neman zabe a jihar Ribas ba tare da izininsa ba za a hukunta shi.

Sai dai Gbara ya kalubalanci Maeba da ya tabbatar da zarginsa da cewa Wike ya bayar da barazana ga duk wanda ke yiwa Atiku yakin neman zabe a jihar.

A cikin wata sanarwa, Gbara ya ce: “Idan har gwamnan yana son yin wannan magana, zai bayyana a hukumance, cewa, a jihar, kada wani ya yi wa Atiku Abubakar yakin neman zabe.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...

Na ki marawa Atiku baya ne saboda juyin yankin Kudu ne – Wike

Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, a wata...

An saki sakamakon jarabawar WASSCE

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma ta fitar da...

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...
X whatsapp