Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers ya bayyana takwaransa na jihar Edo, Godwin Obaseki a matsayin maci amana.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan harin da Obaseki ya kai masa kan adawa da Philip Shaibu, mataimakin gwamnan jihar Edo.
Rikicin ya samo asali ne bayan da shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyoricha Ayu ya ziyarci jihar Edo domin yin sulhu.
Shaibu ya ce, watakila Obaseki da magoya bayansa su fice daga PDP, saboda rikicin da ke cikin jam’iyyar.
Wike ya mayar da martani ya na mai cewa, Shaibu ba shi da kima, domin ya yi barazana ga jam’iyyar adawa.
Da yake kare mataimakinsa, Obaseki ya shaida wa Wike cewa, ba shi ne mai jam’iyyar PDP ba.
Amma da yake jawabi a wajen bude makarantar sakandare a garin Omuanwa, jihar Rivers, a ranar Litinin, Wike ya bayyana Obaseki a matsayin mai butulci.
Ya yi zargin cewa, gwamnan Edo ya ki yin godiya ga jam’iyyar da kuma jama’ar da suka mara masa baya don a zabe shi a lokacin da ya bar jam’iyyar APC.
Wike ya ce, “Idan ka duba jinin Obaseki, abin da za ka gani shine cin amana, da rashin godiya.
“Bari na tsaya yau in nemi gafarar Adams Oshiomhole wanda aka tabbatar mana da cewa za mu ga kalar gaskiya, rashin gaskiya, rashin godiyar Gwamna Obaseki.
“Bari na tsaya yau in nemi gafarar Adams Oshiomhole wanda aka tabbatar mana da cewa za mu ga kalar gaskiya, rashin gaskiya, rashin godiyar Gwamna Obaseki.