fidelitybank

Wike ya kirawo taron gaggawa a kan jam’iyar PDP

Date:

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, a ranar Alhamis ya yi kiran taron gaggawa na masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP reshen jihar.

Wannan dai shi ne irinsa na farko tun bayan dambarwar neman shugabancinsa da rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar a fadin kasar.

Duk da cewa ba a bayyana ajandar taron ba, amma hakan ba zai rasa nasaba da umarnin jihar kan mataki na gaba ba, bayan da Wike da tawagarsa suka fice daga majalisar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar. .

Wadanda aka gayyata zuwa taron dai sun hada da shugabannin jam’iyyar, ‘yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar da wasu ’yan jiga-jigan jam’iyyar.

Ku tuna cewa gwamnan da ya yi imanin cewa an ci amanar sa ne biyo bayan sakamakon zaben fidda gwani na shugaban kasa da kuma na Atiku a yayin da ya ke zabar mataimakinsa a zaben shugaban kasa ya sha alwashin yin magana kan wasu batutuwan da suka haddasa rikicin.

Har ila yau, an ambato Wike yana cewa, “Babu wani abu da ya faru tukuna, amma wani abu zai faru nan ba da jimawa ba.”

Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, wadanda aka gayyata na ci gaba da isa gidan gwamnatin jihar Ribas.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp