fidelitybank

Wike ya gargadi Fubara da kakkausar murya

Date:

Tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike ya yi kira ga gwamna Siminalayi Fubara da ya yi biyayya ga hukuncin kotu idan yana son zaman lafiya a jihar.

Wike ya bayyana hakan ne a ranar Talata a tashar talabijin ta Channels, inda ya ce, “zaman lafiya zai samu ne idan ka yi wa kotu ɗa’a.”

Wannan jawabin na Wike yana zuwa ne bayan zaɓen ƙananan hukumomin jihar, inda kafin zaɓen, wata babbar kotun tarayya ta umarci ƴansanda da DSS su tsame hannunsu daga zaɓen, sannan kada INEC ta ba hukumar zaɓen jihar rajistar masu kaɗa ƙuri’a, duk da cewa wata kotun ta sahale wa hukumar zaɓen jihar gudanar da zaɓen.

Bayan zaɓen ne aka wayi gari da tashin-tashina a jihar, inda har aka ƙona wasu daga cikin hedikwatar ƙananan hukumomi guda uku, lamarin da gwamna Fubara ya ce zai ƙaddamar da bincike domin gano waɗanda suke da hannu.

Wike ya ce, “Lokacin da nake gwamna, ina bin doka da oda na kotu. Bin hukuncin kotu dole ne, bai kamata ka ɗauki doka a hannu ba. Da zarar ka yi kunnen uwar shegu da hukuncin kotu, to kana jawo rikici ne.”

Wike ya ƙara da cewa ana zarginsa da yi wa PDP maƙarƙashiya ta hanyar goyon bayan Tinubu, “amma ga gwamnan ya ɗauki nauyin ƴan takara a APP, sannan shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP ya je rantsar da su.”

A ƙarshe Wike ya ce bai yi da-na-sanin goyon bayan APC a zaɓen 2023 ba.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp