fidelitybank

Wike ya caccaki Atkiu da Bukola Saraki da sauran ‘yan takarar jam’iyar PDP

Date:

Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers ya caccaki tsarin da aka yi na dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP.

Wike ya bayyana tsarin yarjejeniyar a matsayin shara da labaran karya da ake amfani da su wajen yaudarar ‘ya’yan PDP.

Da yake magana da wakilai da mambobin jam’iyyar PDP a Calabar, babban birnin jihar Cross River a ranar Laraba, dan takarar shugaban kasar, ya ce, yarjejeniya ba za ta iya faruwa ba sai ta hanyar adalci da gaskiya.

Ya tuna cewa, ya shaida wa tsohon shugaban majalisar dattawa cewa, ba zai goyi bayan takarar da aka yi a PDP ba.

A cewar Wike: “Ba na nan don wani sharar yarjejeniya. Na gaya wa mutane kada su yaudari ’yan jam’iyyarmu da labaran karya game da yarjejeniya. Dukanmu mun yi imani da yarjejeniya, amma dole ne ya zo da daidaito, adalci, da gaskiya.

“Lokacin da wasu abokan aikina karkashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa suka zo wurina, na ce musu ba zan fada tarkon amincewa ba. Idan kana son tsayawa takara, don Allah ka yi takara, in kuma ba ka shirya ba, don Allah ka koma gida.

“Suna son wanda zai zo ya rusuna musu. Amma abin da kasar ke bukata a yanzu shi ne mutum marar tsoro da jajircewa.”

Irinsu tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar da wasu masu neman tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, sun yi ta kiraye-kirayen neman amincewar dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp