fidelitybank

Wike ya bayar da wa’adi kan masu filaye da gidaje a Abuja su biya haraji ko su bar yankin

Date:

Gwamnatin Tarayya ta bayar da wa’adin ne na kwana 14 rak ga masu filaye da gidajen da ke birnin tarayyar da yawansu ya kai 4,794 waɗanda suka yi biris da ƙin biyan haraji ga filayen.

Ministan babban birnin tarayyar Najeriya Nyesom Ezenwo Wike, ya ce sabon tsarin zai shafi masu filaye da gidaje da kezaune tsakiyar Abuja da aka nemi su biya naira miliyan 5 tare da sauran kuɗaɗen da ake bin su bashi a baya. Sai masu kadarorin a Maitama da Asokoro da Wuse II da Guzape, su kuma za su biya harajin naira miliyan 3, yayin da masu filayen da ke Wuse I da Garki I da Garki II an dora mu su biyan naira miliyan 2.

Ministan ya ce wannan mataki ne da gwamnatin ƙasar ta fito da shi domin tabbatar da masu filaye sun kiyaye dokokin biyan haraji da kuma tafiyar da su yadda ya dace.

Haka ma ministan birnin tarayyar Najeriyar ya ce za su ɗauki matakin ladaftar da waɗanda suka mallaki gidaje da sauran kadarorin da ba su yi musu rajista ba, inda su ma aka ba su wa’adin kwana 14 da su yi wa filayen da sauran kadarorin rajista kafin cikar wa’adin ko su fuskanci ƙwacewa.

Mista Wike ya ce matakan da gwamnatin tarayya na buƙatar a tabbatar da an biya harajin dukan gidaje da filaye akan lokaci kasancewar abu ne mai muhimmanci a ɓangaren bunƙasa birnin na Abuja tare da samar da aikin yi ga jama’a.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...
X whatsapp