fidelitybank

Wike ya bayar da wa’adi kan masu filaye da gidaje a Abuja su biya haraji ko su bar yankin

Date:

Gwamnatin Tarayya ta bayar da wa’adin ne na kwana 14 rak ga masu filaye da gidajen da ke birnin tarayyar da yawansu ya kai 4,794 waɗanda suka yi biris da ƙin biyan haraji ga filayen.

Ministan babban birnin tarayyar Najeriya Nyesom Ezenwo Wike, ya ce sabon tsarin zai shafi masu filaye da gidaje da kezaune tsakiyar Abuja da aka nemi su biya naira miliyan 5 tare da sauran kuɗaɗen da ake bin su bashi a baya. Sai masu kadarorin a Maitama da Asokoro da Wuse II da Guzape, su kuma za su biya harajin naira miliyan 3, yayin da masu filayen da ke Wuse I da Garki I da Garki II an dora mu su biyan naira miliyan 2.

Ministan ya ce wannan mataki ne da gwamnatin ƙasar ta fito da shi domin tabbatar da masu filaye sun kiyaye dokokin biyan haraji da kuma tafiyar da su yadda ya dace.

Haka ma ministan birnin tarayyar Najeriyar ya ce za su ɗauki matakin ladaftar da waɗanda suka mallaki gidaje da sauran kadarorin da ba su yi musu rajista ba, inda su ma aka ba su wa’adin kwana 14 da su yi wa filayen da sauran kadarorin rajista kafin cikar wa’adin ko su fuskanci ƙwacewa.

Mista Wike ya ce matakan da gwamnatin tarayya na buƙatar a tabbatar da an biya harajin dukan gidaje da filaye akan lokaci kasancewar abu ne mai muhimmanci a ɓangaren bunƙasa birnin na Abuja tare da samar da aikin yi ga jama’a.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp