Gwamnatin Tarayya ta bayar da wa’adin ne na kwana 14 rak ga masu filaye da gidajen da ke birnin tarayyar da yawansu ya kai 4,794 waɗanda suka yi biris da ƙin biyan haraji ga filayen.
Ministan babban birnin tarayyar Najeriya Nyesom Ezenwo Wike, ya ce sabon tsarin zai shafi masu filaye da gidaje da kezaune tsakiyar Abuja da aka nemi su biya naira miliyan 5 tare da sauran kuɗaɗen da ake bin su bashi a baya. Sai masu kadarorin a Maitama da Asokoro da Wuse II da Guzape, su kuma za su biya harajin naira miliyan 3, yayin da masu filayen da ke Wuse I da Garki I da Garki II an dora mu su biyan naira miliyan 2.
Ministan ya ce wannan mataki ne da gwamnatin ƙasar ta fito da shi domin tabbatar da masu filaye sun kiyaye dokokin biyan haraji da kuma tafiyar da su yadda ya dace.
Haka ma ministan birnin tarayyar Najeriyar ya ce za su ɗauki matakin ladaftar da waɗanda suka mallaki gidaje da sauran kadarorin da ba su yi musu rajista ba, inda su ma aka ba su wa’adin kwana 14 da su yi wa filayen da sauran kadarorin rajista kafin cikar wa’adin ko su fuskanci ƙwacewa.
Mista Wike ya ce matakan da gwamnatin tarayya na buƙatar a tabbatar da an biya harajin dukan gidaje da filaye akan lokaci kasancewar abu ne mai muhimmanci a ɓangaren bunƙasa birnin na Abuja tare da samar da aikin yi ga jama’a.