Gwamna Nyesom Wike ya bayyana dalilinsa na amincewa da filin wasa na Adokiye Amiesimaka na yakin neman zaben Atiku Abubakar a jihar Ribas.
Da yake magana a ranar Talata, 7 ga watan Fabrairu, Wike ya ce, ya yanke shawarar bayar da wurin gudanar da gangamin ne bayan wasu mutanen da bai ambaci sunayensu ba sun yi masa raddi, kamar yadda PM News ta ruwaito.
Karanta Wannan:Â Ban kama magoya bayan Atiku ba – Wike
Gwamnan ya ce ba ya son a rubuta cewa jam’iyyar PDP ta sha kaye a jihar sa saboda ya ki amincewa da filin wasan don amfani da shi.