Jam’iyyar People’s Democratic Party, PDP ta gudanar da wani gangami na jam’iyyar, domin tallafa wa dan takararta a zaben gwamnan Osun da ke tafe, Ademola Nurudeen Jackson Adeleke.
Dukkan jiga-jigan jam’iyyar da masu ruwa da tsaki na jihar in ban da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike da tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose.
Sauran wadanda ba su halarci wurin taron sun hada da gwamnan jihar Abia, Okezie Ikpeazu, gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde.
Idan dai za a iya tunawa jam’iyyar ta fada cikin rikici tun bayan bayyanar Ifeanyi Okowa a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar.
POLITICS NIGERIA ta ruwaito cewa, kwamitin da ya kafa domin tantance dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Atiku Abubakar ya zabi Wike amma abin mamaki shugabannin jam’iyyar da tsohon mataimakin shugaban kasar sun ki amincewa da shi.
Hakan bai yiwa gwamnan jihar Benuwe Samuel Ortom dadi ba, inda yayi gaggawar nuna rashin jin dadinsa da ci gaban da aka samu tare da yin kira ga jam’iyyar da ta tuntubi Wike.
A makon da ya gabata ne wasu gwamnonin APC uku tare da Fayose suka ziyarci Wike a Fatakwal domin lallashinsa zuwa jam’iyya mai mulki da kuma abubuwan da suka faru a yau, ga dukkan alamu rikicin jam’iyyar adawa ya yi nisa.