Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya ce, gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas ya bayyana karara cewa, ba shi da sha’awar zama mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben 2023 mai zuwa.
Jam’iyyar adawa ta tsunduma cikin rikici ne biyo bayan sakamakon zaben fidda gwanin ta na shugaban kasa da kuma fitowar gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa a matsayin abokin takararta na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, lamarin da ya sa jam’iyyar ta fara sulhuntawa.
Wasu jiga-jigan jam’iyyar da suka hada da gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, da tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, sun soki yadda jam’iyyar ta gudanar da zaben fidda gwani, da yadda Wike ya yi da kuma zaben wanda zai tsaya takara a PDP.
Sai dai Lamido ya bayyana cewa, Wike, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ya ce, ba ya amfani da zaben fidda gwanin ne wajen yin shawarwarin neman mataimaki.