fidelitybank

WHO ta amince da rigakafin farko ta Cutar ƙyandar biri

Date:

Hukumar Lafiya ta duniya ta sanar da amincewa da allurar rigakafin ƙyandar biri na farko.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da aka kai rigakafin MVA-BN zuwa ƙasar DR Congo, ƙasar da cutar ta fi ƙamari.

Akwai kusan mutum 22,000 da suka kamu da cutar a Congo, sannan aƙalla mutum 716 ne suka rasu a yanayi mai kama da cutar.

Zuwa yanzu, an kai rigakafin guda 200,000 zuwa ƙasar ta DR Congo daga Tarayyar Turai, sannan an kai guda 50,000 daga Amurka.

Wata ƙwayar cuta da ake iya yaɗawa daga dabbobi zuwa mutane, sannan mutane na iya yaɗawa zuwa wasu ne ke jawo cutar ta Mpox.

Cutar na jawo zazzaɓi da ƙuraje, sannan a wasu lokuta tana kisa.

WHO ta wallafa a shafinta na X a ranar Litinin cewa, “amincewa da wannan rigakafin zai taimaka a yaƙin da ake yi da annobar cutar ƙyandar biri a Afrika, da kuma kare dawowar cutar a gaba,” kamar yadda Shugaban WHO, Tedros Adganom Ghebreyesus ya bayyana a sanarwar.

“Yanzu abun da muke buƙata shi ne a haɗa da yawa, a samu saya sannan a raba domin sauƙaƙa samuwarsa a wuraren da ake buƙata domin daƙile yaɗuwar cutar da kare rayukan al’umma.”

Amincewar WHO na nufin duba ingancin allura da sauran magunguna, wanda hakan ke ba Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙungiyoyin duniya damar saya da raba su.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp