fidelitybank

WHO ta amince da rigakafin farko ta Cutar ƙyandar biri

Date:

Hukumar Lafiya ta duniya ta sanar da amincewa da allurar rigakafin ƙyandar biri na farko.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da aka kai rigakafin MVA-BN zuwa ƙasar DR Congo, ƙasar da cutar ta fi ƙamari.

Akwai kusan mutum 22,000 da suka kamu da cutar a Congo, sannan aƙalla mutum 716 ne suka rasu a yanayi mai kama da cutar.

Zuwa yanzu, an kai rigakafin guda 200,000 zuwa ƙasar ta DR Congo daga Tarayyar Turai, sannan an kai guda 50,000 daga Amurka.

Wata ƙwayar cuta da ake iya yaɗawa daga dabbobi zuwa mutane, sannan mutane na iya yaɗawa zuwa wasu ne ke jawo cutar ta Mpox.

Cutar na jawo zazzaɓi da ƙuraje, sannan a wasu lokuta tana kisa.

WHO ta wallafa a shafinta na X a ranar Litinin cewa, “amincewa da wannan rigakafin zai taimaka a yaƙin da ake yi da annobar cutar ƙyandar biri a Afrika, da kuma kare dawowar cutar a gaba,” kamar yadda Shugaban WHO, Tedros Adganom Ghebreyesus ya bayyana a sanarwar.

“Yanzu abun da muke buƙata shi ne a haɗa da yawa, a samu saya sannan a raba domin sauƙaƙa samuwarsa a wuraren da ake buƙata domin daƙile yaɗuwar cutar da kare rayukan al’umma.”

Amincewar WHO na nufin duba ingancin allura da sauran magunguna, wanda hakan ke ba Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙungiyoyin duniya damar saya da raba su.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp