An yi imanin tsohon dan wasan Faransa, Zinedine Zidane, zai fi son komawa Manchester United a kan Bayern Munich.
Marca ta ruwaito cewa Zidane yana ba da lokacinsa don yanke shawara.
Tsohon dan wasan mai shekaru 51 ya fito a matsayin wanda zai maye gurbin Thomas Tuchel a Bayern.
Tun da ya bar Madrid a shekara ta 2021 Zidane bai jagoranci wata kungiya ba amma mutum ne da ake bukata.
A lokacin da ya ke Bernabeu, Bafaranshen ya lashe kofin zakarun Turai sau uku a jere a karon farko.
Amma a baya akwai shakku game da gudanar da kungiyoyi a wajen Faransa, Spain ko Italiya, saboda ba ya jin Turanci ko Jamusanci.
Amma rahotanni a Spain a ranar Juma’a sun ce Zidane ya kasance “taki daya” daga yarjejeniyar komawa Bayern a bazara, tare da hukumar Bayern ta amince da cewa shi ne mafi kyawun dan takara da ya rage.