fidelitybank

Watakil Wike ya ficce daga PDP zuwa APC – Joe Igbokwe

Date:

Wani jigo a jam’iyyar APC, Joe Igbokwe, ya kara zafafa rade-radin cewa, gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike na iya ficewa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) zuwa APC.

Yayin da ake ta rade-radin yiwuwar sauya shekar Wike daga PDP zuwa APC, Igbokwe a shafinsa na Facebook a safiyar ranar Litinin, ya raba hoton gwamnan Ribas da takwaransa na jihar Ebonyi, David Umahi.

Da yake raba hoton, Igbokwe ya kara da wani rubutu da ke cewa: “ABUBUWAN DA AKE LOKA ANAN KUMA BA ZAN FADA MUKU BA.”

Naija News ta rawaito cewa, Umahi da kansa ya na jam’iyyar PDP ne har zuwa lokacin da ya koma APC a kwanakin baya.

Idan dai za a iya tunawa, bayan da Atiku Abubakar ya fara rasa tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a shekarar 2023, daga bisani kuma, dan takarar gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Delta, ya yi ta rade-radin cewa Wike na iya barin PDP zuwa wata jam’iyya.

A ranar Asabar ne gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi ya isa birnin Fatakwal inda ya gana da shi a wata ziyarar sada zumunci da ‘yan uwantaka’ da misalin karfe 9 na dare.

Ziyarar Umahi ta zama ganawa ta farko da Wike bayan da tsohon ya fice daga PDP zuwa APC sakamakon rashin gamsuwa da jam’iyyar.

Wani kodinetan kungiyar goyon bayan Tinubu a Kudu-maso-Kudu, Gabriel Abijah, a wata hira da yayi da Siyasar Najeriya, yayi ikirarin cewa nan bada jimawa ba Wike zai koma APC.

Sai dai kuma mai taimaka wa gwamna Nyesom Wike kan harkokin yada labarai, Kelvin Ebiri a ranar Larabar da ta gabata ya bayyana cewa gwamnan jihar Ribas ba zai taba barin jam’iyyar Peoples Democratic Party ba.

A cewar Ebiri, ya ce, an yi amfani da wani faifan bidiyo da ke nuna cewa Wike na barazanar shiga jam’iyyar All Progressives Congress.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp