Injiniya Muaz Magaji Dan Sarauniya ya sanar da ficewarsa daga jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance, inda ya bukaci dukkan jam’iyyun siyasa da su shaida haka, daga rana irinta yau.
Tsohon Kwamishinan ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafin sa na Facebook a safiyar asabar din nan.
Dan Sarauniya bai bayyana jam’iyyar da ya koma ba, amma ana ganin hakan na da nasara da rashin jituwarsa da Gwamnatin Kano Wanda har ta yi sanadiyyar kai shi kotu.
Ko a jiya an hango tsohon kwamishinan na ayyukan a jihar Kano, ya ziyarci Sanata Bello Hayatu Gwarzo, wanda jigo ne a jam’iyyar PDP tsagin Ambasada Aminu Wali, ya kuma umarci magoya bayansa dasu tuntubi shugabannin PDP na mazabunsu, domin jin halin da jam’iyyar ke ciki.