fidelitybank

Wata shida kacal zan kawar da ƴan ta’adda a Najeriya – Wike

Date:

Gwamnan jihar Rivers kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Nyesom Wike, ya sha alwashin kawar da ‘yan ta’adda a cikin watanni shida idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a shekarar 2023.

Wike ya ce ya zana tsarin ne domin samar da kayan aiki da na’urorin da suka dace da hukumomin tsaro a gaggauta kawo karshen ‘yan fashi a kasar.

Wike, wanda ya yi magana a wani taro a Abeokuta da wakilan PDP daga jihar Ogun, ya ce, zai ba da fifiko wajen kare rayuka da dukiyoyin kowane mutum.

Ya ce: “Da zarar an samu rashin tsaro ba za ka iya yin komai ba. Dole ne ku sami kwanciyar hankali don masu zuba jari su shigo, don mutane su kafa masana’antu. Don haka babban abin da ke cikin watanni shida na farko a matsayina na shugaban Najeriya shi ne kawo karshen ‘yan fashi.
Duk wadancan barayin; bari su jira ni. Zan bi su. Aikina ne. Zan samar wa jami’an tsaro duk abin da suke bukata.”

Wike a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Kelvin Ebiri ya sanya wa hannu, ya ce, kasar na fatan samun shugaba mai karfi, jajirtacce kuma mara tsoro irinsa don magance matsalar tsaro da ake fama da ita.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp