Gwamnan jihar Rivers kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Nyesom Wike, ya sha alwashin kawar da ‘yan ta’adda a cikin watanni shida idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a shekarar 2023.
Wike ya ce ya zana tsarin ne domin samar da kayan aiki da na’urorin da suka dace da hukumomin tsaro a gaggauta kawo karshen ‘yan fashi a kasar.
Wike, wanda ya yi magana a wani taro a Abeokuta da wakilan PDP daga jihar Ogun, ya ce, zai ba da fifiko wajen kare rayuka da dukiyoyin kowane mutum.
Ya ce: “Da zarar an samu rashin tsaro ba za ka iya yin komai ba. Dole ne ku sami kwanciyar hankali don masu zuba jari su shigo, don mutane su kafa masana’antu. Don haka babban abin da ke cikin watanni shida na farko a matsayina na shugaban Najeriya shi ne kawo karshen ‘yan fashi.
Duk wadancan barayin; bari su jira ni. Zan bi su. Aikina ne. Zan samar wa jami’an tsaro duk abin da suke bukata.”
Wike a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Kelvin Ebiri ya sanya wa hannu, ya ce, kasar na fatan samun shugaba mai karfi, jajirtacce kuma mara tsoro irinsa don magance matsalar tsaro da ake fama da ita.