Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana jam’iyyar APC mai mulki a matsayin wadda ta lashe zaben karamar hukumar Abaji da ke Abuja.
Shi ne yanki na biyu da jam’iyya mai mulki ta samu, bayan Gwagwalada.
Jami’in zabe na INEC a Abaji, Farfesa Gabriel Mordi, wanda ya bayyana sakamakon zaben a ofishin hukumar a ranar Lahadi, ya ce, dan takarar jam’iyyar APC da har yanzu ba a san shi ba ya samu kuri’u 7,289.
Ya doke jam’iyyar adawa ta PDP, Alhaji Yahaya Garba Gawu, wanda ya samu kuri’u 4,062