fidelitybank

Wata Mata ta maka Mijinta a kotun Kaduna saboda yaƙi kai ta Saudiyya

Date:

Wata mata mai shekaru 45, mai suna Karima Nuhu, a ranar Talata ta maka mijinta, Musa Falalu, a gaban wata kotun shari’ar musulunci da ke Rigasa, a jihar Kaduna, bisa zargin kin kai ta ƙasar Saudiyya.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya ruwaito cewa, matar wadda ke zaune a unguwar Rigasa, ta shaida wa kotun cewa ta yi aure da Falalu tsawon shekara huɗu, amma abinci na tsawon wata biyu kaɗai ya ba ta tun bayan yin auren.

“Ya faɗa min cewa ya rasa aikinsa na direba amma ya samu wani a Saudiyya, inda ya bukace ni da in yi hakuri da kuma yin alkawarin tafiya da ni,” in ji matar.

“A yanzu, ni ke ciyar da kaina. Har ma na aro masa kuɗi domin ya samu biyan kudin tafiyar, amma bayan samun abin da yake so sai ya sake ni,” inji ta.

Ta shaida wa kotun cewa Allah zai mata sakayya tsakaninta da mijin a gobe kiyama.

Sai dai wanda ake tuhumar ya musanta zargin, inda ya shaida wa kotu cewa ya saki matar tasa.

Alkalin kotun, Malam Anass Khalifa, wanda ya tabbatar da rabuwar aure tsakanin ma’auratan, ya ce kotun za ta saurari korafe-korafen matar ne idan da a ce ta gansu.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp