Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Ondo, ta tarbi wasu ‘ya’yan jam’iyyar PDP a karamar hukumar Idanre.
Mambobin jam’iyyar SDP da ke yankin su ma sun koma jam’iyya mai mulki.
Masu sauya shekar sun bayyana rashin tabuka komai na tsoffin jam’iyyunsu a zaben da ya gabata a matsayin dalilin da ya sa suka yanke shawarar komawa APC.
A cewarsu, rashin gamsuwarsu da yadda jam’iyyunsu na baya ba su iya tafiyar da al’amuransu yadda ya kamata ya tilasta musu neman wata hanyar siyasa ta daban.
Farfesa John Jejelola wanda ya yi magana a madadin wadanda suka sauya sheka ya bayyana cewa an ruguza tsarin jam’iyyar PDP da SDP a Idanre tare da hadewa da APC.
Ya bayyana cewa matakin zai karfafa karfin jam’iyya mai mulki a jihar, tare da raunana kafar ‘yan adawa.
Da yake karin haske kan nasarorin da shugaban jam’iyyar APC na jihar, Ade Adetimehin dan asalin karamar hukumar Jejelola ya samu, ya jaddada muhimmiyar rawa da Adetimehin ya taka wajen jawo wadanda suka sauya sheka zuwa APC.
Da yake karbar wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyarsa, Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Adetimehin, wanda shi ma dan karamar hukumar Idanre ne, ya bayyana cewa jiga-jigan jam’iyyar PDP da suka sauya sheka zuwa jam’iyyarsa, su ne mutanen da a kodayaushe suke ba shi da jam’iyyarsa wahala a lokacin zabe.
Ya bayyana cewa da sauya shekar su zuwa jam’iyyar sa APC za ta yi ranar fage a duk zabukan kananan hukumomi.