Alamu na nuna cewa wasu jihohin ba za su kada kuri’a ba, a babban taron jam’iyyar All Progressives Congress na kasa da ke gudana a Abuja.
Jihohin sun hada da Akwa Ibom, Bayelsa da kuma Taraba.
Zaben kwamitocin zartaswa na jahohin da abin ya shafa dai na fuskantar shari’a a kotu, don haka jam’iyyar a jihohin.
Sai dai kuma arahotanni na cewa, za a ba wa wakilai da abun ya shafa damar kada kuri’a, yayin da wakilan da suka fito daga majalisun da aka gudanar a jihohin da abin ya shafa ba za su kada kuri’a ba.