fidelitybank

Wani Ɗalibi ya mutu yayin da aka sa shi tsallan Kwaɗo 162 a jihar Ogun

Date:

An samu tashin hankali a karamar hukumar Imeko Afon ta jihar Ogun, yayin da wani dalibi mai suna Ariyo Monday ya rasu bayan da wani malami ya yi masa bulala tare da neman ya yi tsallen kwadi 162.

Ariyo, dalibin makarantar Obafemi Grammar School, ya rasu ranar Juma’a.

Kamar yadda wani faifan bidiyo da wani mai fafutuka, Justadetoun ya wallafa a yanar gizo, ya bayyana cewa malamin ya dauki kwandon shara ya je ajin Ariyo ya ce wa daliban kada su fasa, amma marigayin cikin zolaya ya amsa wa malamin da wasa, inda ya ce an sayo kwandon da kudin daliban.

Ta bayyana cewa martanin da ya bayar ya bata wa malamin rai, inda ya kai kara ga shugaban makarantar kuma aka ba shi umarnin hukunta marigayin.

Justadetoun ya bayyana cewa, an yi wa Ariyo bulala 164 na sandar, kuma ana cikin haka sai ya fadi kasa.

Rahotanni daga faifan bidiyon cewa Ariyo da aka dora a kan drip tana nishi tana ta faman magana daga kan gadon asibiti.

A halin da ake ciki, kakakin rundunar ‘yan sandan, Omolola Odutola, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a yammacin ranar Juma’a, ya ce sabanin rahotan, an yi wa marigayin dukan tsiya da sara 24, inda aka yi ta tsallen kwadi 162.

Odutola ya ce ya rasu ne a cibiyar lafiya ta tarayya dake Abeokuta.

Ta ce, “Lamarin ya faru ne a ranar 15 ga Oktoba, 2024. An bukaci marigayin ya yi tsallen kwadi 162, kuma an yi masa bulala 24 na rake. An garzaya da shi FMC Idi-Aba domin kula da lafiyarsa, kuma ya rasu yau (Juma’a).

PRO ya bayyana cewa an ajiye gawar a dakin ajiyar gawarwaki na Ayetoro domin a tantance gawarwakin kuma har yanzu ana ci gaba da binciken musabbabin mutuwar.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp