Hukumomi a jihar Borno sun tabbatar da cewa, mafarauta sun bindige wani Zaki da ya gilma ta wani kauye a yankin Konduga.
Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, kamar yadda daraktan Kula da Gandun Daji da Namun Daji na jihar, Ayuba Peter ya shaidawa BBC.
Rahotanni sun ce Zakin ya ga ta kansa ne a lokacin da mafarauta suka yi artabu da shi tun a lokacin.