fidelitybank

Wani ya yi yunkurin hallaka kansa a gaban Ka’aba

Date:

Jami’an tsaro na musamman da ke kula da Masallacin Harami da ke birnin Makkah sun fara gudanar da bincike kan mutum da ya yi yunkurin halaka kansa, inda ya hau bene na sama na Masallacin domin ya faɗo ƙasa.

An garzaya da mutumin zuwa asibiti domin samun kulawar da ta dace, sai dai ba a bayyana ƙasar da ya fito ba.

Rundunar ta musamman mai kula da tsaron masallacin Harami ta bayyana a shafinta na X cewa “an kammala binciken da ya kamata,” amma babu wani ƙarin bayani kan lamarin.

A shekarar 2018, wani mahajjaci mai shekaru 26 ya kashe kansa a Masallacin Harami, lamarin da ya haifar da firgici da fargaba a tsakanin alhazai da masu ibada a Masallacin.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan Makkah ya bayyana a watan Yunin 2018 cewa jami’an tsaro sun fara gudanar da bincike kan wani lamari, inda wani mahajjaci ya yi tsalle daga kan wani rufi a unguwar Mas’a ya kuma faɗo ƙasa, abin da ya yi sanadiyyar rasa ransa.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp